Publicidade

Salmos 124

Waƙar haurawa. Ta Dawuda.

1 Da ba don Ubangiji ya kasance a gefenmu ba,

bari Isra’ila yă ce,

2 da ba don Ubangiji ya kasance a gefenmu ba

sa’ad da aka auka mana,

3 sa’ad da fushinsu ya ƙuna a kanmu,

ai, da sun haɗiye mu da rai;

4 da rigyawa ta kwashe mu,

da ambaliya ta rufe mu.

5 Da ruwa mai hauka

ya share mu ƙaf.

6 Yabo ya tabbata ga Ubangiji,

wanda bai bari aka yayyage mu da haƙoransu ba.

7 Mun tsira kamar tsuntsu

daga tarkon mai farauta;

an tsinke tarko,

muka kuwa tsira.

8 Taimakonmu yana a sunan Ubangiji,

Wanda ya yi sama da ƙasa.

Veja também

Publicidade
Bíblia Online Bíblia Online

Bíblia Online • Versão: 2026-06-16_06-50-08-