Publicidade

Salmos 19

Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda.

1 Sammai suna shelar ɗaukakar Allah;

sararin sama suna furta aikin hannuwansa.

2 Kowace rana tana yin jawabi;

kowane dare yana nuna sani.

3 Ba magana, ba kalmar da aka hurta,

ba wani amon da aka ji daga gare su.

4 Duk da haka muryarsu tana kaiwa ga dukan duniya,

kalmominsu zuwa iyakokin duniya.

A sammai Allah ya kafa tenti domin rana,

5 wanda yake kamar ango mai fitowa daga rumfarsa,

kamar gwani ɗan wasan da yake farin ciki yă yi tsere.

6 Takan taso daga ƙarshen sammai

ta kewaye zuwa wancan;

babu abin da yake ɓuya wa zafinta.

7 Dokar Ubangiji cikakkiya ce,

takan wartsakar da rai.

Farillan Ubangiji abin dogara ne,

suna mai da hikima da sauƙi.

8 Ƙa’idodin Ubangiji daidai ne,

suna ba da farin ciki ga zuciya.

Umarnan Ubangiji haske ne

suna ba da haske ga idanu.

9 Tsoron Ubangiji yakan kawo tsabtar zuciya,

zai kasance har abada.

Farillan Ubangiji tabbatattu ne,

kuma gaba ɗaya masu adalci ne.

10 Sun fi zinariya daraja,

fiye da zalla zinariya nesa;

sun fi zuma zaƙi

fiye da zuma daga kaki.

11 Ta wurinsu ana gargaɗe bawanka;

a kiyaye su akwai lada mai girma.

12 Wane ne zai iya rabe kurakuransa?

Ya gafarta ɓoyayyun laifofinsa.

13 Ka kiyaye bawanka daga zunubin ganganci;

kada ka bari su yi mulki a kaina.

Ta haka zan zama marar laifi;

marar laifi na babban tawaye.

14 Bari kalmomin bakina da tunanin zuciyata

su zama abin gamsuwa a gabanka,

Ya Ubangiji, Dutsena da Mai fansata.

Veja também

Publicidade
Bíblia Online Bíblia Online

Bíblia Online • Versão: 2026-06-16_06-50-08-