Publicidade

Salmos 63

Zabura ta Dawuda. Sa’ad da yake a hamadar Yahuda.

1 Ya Allah, kai ne Allahna,

da nacewa na neme ka;

raina yana ƙishinka,

jikina yana marmarinka,

cikin busasshiyar ƙasar da ta zozaye

inda babu ruwa.

2 Na gan ka a wuri mai tsarki

na kuma dubi ikonka da ɗaukakarka.

3 Domin ƙaunarka ta fi rai kyau,

leɓunana za su ɗaukaka ka.

4 Zan yabe ka muddin raina,

kuma a cikin sunanka zai ɗaga hannuwana.

5 Raina zai ƙoshi kamar da abinci mafi kyau;

da leɓunan rerawa bakina zai yabe ka.

6 A gadona na tuna da kai;

ina tunaninka dukan dare.

7 Domin kai ne mai taimakona,

ina rera a cikin inuwar fikafikanka.

8 Raina ya manne maka;

hannunka na dama yana riƙe da ni.

9 Su da suke neman raina za su hallaka;

za su gangara zuwa zurfafan duniya.

10 Za a bayar da su ga takobi

su kuma zama abincin karnukan jeji.

11 Amma sarki zai yi farin ciki ga Allah;

dukan waɗanda suke rantse da sunan Allah za su yabe shi,

amma za a rufe bakunan maƙaryata.

Veja também

Publicidade
Bíblia Online Bíblia Online

Bíblia Online • Versão: 2026-06-16_06-50-08-