Publicidade

Salmos 28

Ta Dawuda.

1 A gare ka nake kira,

ya Ubangiji Dutsena;

kada ka yi mini kunnen ƙashi.

Gama in ka yi shiru,

zan zama kamar waɗanda suka gangara rami.

2 Ka ji kukata ta neman jinƙai

yayinda nake kira ka don neman taimako,

yayinda nake daga hannuwana

wajen Wurinka Mafi Tsarki.

3 Kada ka ja ni tare da mugaye,

tare da masu yin mugunta,

masu magana kamar ta alheri ce da maƙwabtansu

amma suna riƙe da su a zukatansu.

4 Ka sāka musu da ayyukansu

da kuma don mugun aikinsu;

ka sāka musu saboda abin da hannuwansu suka yi

ka kuma mayar musu abin da ya dace da su.

5 Da yake ba su kula da ayyukan Ubangiji

da abin da hannuwansa suka yi ba,

zai rushe su

ba kuwa zai ƙara gina su ba.

6 Yabo ya tabbata ga Ubangiji,

gama ya ji kukata na neman jinƙai.

7 Ubangiji shi ne ƙarfina da garkuwata;

zuciyata ta amince da shi, kuma na sami taimako.

Zuciyata ta yi tsalle don farin ciki

zan kuwa yi godiya gare shi cikin waƙa.

8 Ubangiji shi ne ƙarfin mutanensa,

kagarar ceto domin shafaffensa.

9 Ka cece mutanenka ka kuma albarkace gādonka;

ka zama mai kiwonsu ka kuma riƙe su har abada.

Veja também

Publicidade
Bíblia Online Bíblia Online

Bíblia Online • Versão: 2026-06-18_10-32-54-