Pular para o conteúdo
Publicidade

Zabura 131

Waƙar haurawa. Ta Dawuda.

1 Zuciyata ba mai girman kai ba ce, ya Ubangiji,

idanuna ba sa fariya;

ban dami kaina da manyan al’amura ba

ko abubuwan da suka sha ƙarfina.

2 Amma na haƙura na kuma kwantar da raina;

kamar yaron da aka yaye tare da mahaifiyarsa,

kamar yaron da aka yaye haka raina yake a cikina.

3 Ya Isra’ila, sa zuciyarka ga Ubangiji

yanzu da har abada kuma.

Estes versículos te tocaram? Ore agora!

+581 estão orando agora.

Junte-se à corrente de oração.

Veja também