Publicidade

Salmos 79

Zabura ta Asaf.

1 Ya Allah, al’ummai sun mamaye gādonka;

sun ƙazantar da haikalinka mai tsarki,

sun bar Urushalima kufai.

2 Sun ba da gawawwakin bayinka

kamar abinci ga tsuntsayen sararin sama,

nama jikin tsarkakanka ga namun jejin duniya.

3 Sun zubar da jini kamar ruwa

ko’ina a Urushalima,

kuma babu wani da zai binne matattu.

4 Mun zama abin reni ga maƙwabta,

abin ba’a da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.

5 Har yaushe, ya Ubangiji za ka yi ta fushi? Har abada ne?

Har yaushe kishinka zai yi ta ƙuna kamar wuta?

6 Ka zuba fushinka a kan al’umman

da ba su yarda da kai ba,

a kan mulkokin

da ba sa kira bisa sunanka;

7 gama sun cinye Yaƙub

suka lalatar da ƙasar zamansa.

8 Kada ka riƙe zunubai kakanni a kanmu;

bari jinƙanka yă zo da sauri yă sadu da mu,

gama mun fid da zuciya sarai.

9 Ka taimake mu, ya Allah Mai Cetonmu,

saboda ɗaukakar sunanka;

ka cece mu ka kuma gafarta mana zunubanmu

saboda sunanka.

10 Don me al’ummai za su ce,

"Ina Allahnsu yake?"

A idanunmu, ka sanar wa al’ummai

cewa kana ɗaukan fansar jinin bayinka da aka zubar.

11 Bari nishe-nishen ’yan kurkuku su zo gabanka;

ta wurin ƙarfin hannunka ka kiyaye waɗanda aka yanke wa hukuncin mutuwa.

12 Ka sāka a cinyoyin maƙwabtanmu sau bakwai

zage-zagen da suka yi ta yi maka, ya Ubangiji.

13 Sa’an nan mu mutanenka, tumakin makiyayarka,

za mu yabe ka har abada;

daga tsara zuwa tsara

za mu yi ta ba da labarin yabonka.

Veja também

Publicidade
Bíblia Online Bíblia Online

Bíblia Online • Versão: 2026-06-16_18-40-07-