Publicidade

Salmos 130

Waƙar haurawa.

1 Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;

2 Ya Ubangiji, ka ji muryata.

Bari kunnuwanka su saurara

ga kukata ta neman jinƙai.

3 In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai,

Ya Ubangiji, wa zai tsaya?

4 Amma tare da kai akwai gafartawa,

saboda haka ake tsoronka.

5 Zan jira Ubangiji, raina zai jira,

kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.

6 Raina na jiran Ubangiji

fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya,

fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.

7 Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji,

gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa

kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.

8 Shi kansa zai fanshi Isra’ila

daga dukan zunubansu.

Veja também

Publicidade
Bíblia Online Bíblia Online

Bíblia Online • Versão: 2026-06-18_14-04-22-