Publicidade

Salmos 64

Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda.

1 Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna;

ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.

2 Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye,

daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.

3 Sukan wāsa harsunansu kamar takuba

su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.

4 Sukan yin kwanto su harbi marar laifi;

sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.

5 Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu,

sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu;

su ce, "Wa zai gan su?"

6 Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce,

"Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!"

Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.

7 Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi;

nan da nan za a buge su su fāɗi.

8 Zai juya harshensu a kansu

yă kuma kawo su ga hallaka;

duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.

9 Dukan mutane za su ji tsoro;

za su yi shelar ayyukan Allah

su kuma yi tunanin abin da ya aikata.

10 Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji

su kuma nemi mafaka a gare shi;

bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!

Veja também

Publicidade
Bíblia Online Bíblia Online

Bíblia Online • Versão: 2026-06-16_06-50-08-