Publicidade

Salmos 4

Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda.

1 Ka amsa mini sa’ad da na kira gare ka,

Ya Allahna mai adalci.

Ka ba ni sauƙi daga wahalata;

ka ji tausayina ka kuma ji addu’ata.

2 Har yaushe, ya ku mutane za ku mai da ɗaukakata abin kunya?

Har yaushe za ku ƙaunaci ruɗu ku nemi allolin ƙarya? Sela

3 Ku san cewa Ubangiji ya keɓe masu tsoron Allah wa kansa;

Ubangiji zai ji sa’ad da na yi kira gare shi.

4 Cikin fushinku kada ku yi zunubi;

sa’ad da kuke kan gadajenku,

ku bincike zukatanku ku kuma yi shiru. Sela

5 Ku miƙa hadayun da suka dace

ku kuma dogara ga Ubangiji.

6 Yawanci suna cewa, "Wa zai yi mana alheri?"

Bari hasken fuskarka yă haskaka a kanmu, ya Ubangiji.

7 Ka cika zuciyata da farin ciki

sa’ad da hatsinsu da sabon ruwan inabinsu ya yi yawa.

8 Zan kwanta in kuma yi barci lafiya,

gama kai kaɗai, ya Ubangiji,

kake sa mazaunina yă kasance lafiya lau.

Veja também

Publicidade
Bíblia Online Bíblia Online

Bíblia Online • Versão: 2026-06-15_21-32-39-