Publicidade

Salmos 29

Zabura ta Dawuda.

1 Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya,

ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.

2 Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa;

ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.

3 Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye;

Allah Maɗaukaki ya yi tsawa,

Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.

4 Muryar Ubangiji mai iko ce;

muryar Ubangiji da girma take.

5 Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon.

Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.

6 Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi,

Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.

7 Muryar Ubangiji ta buga

da walƙatar walƙiya.

8 Muryar Ubangiji ta girgiza hamada

Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.

9 Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya sa barewa ta haihu.

ya kakkaɓe itatuwan kurmi.

Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, "Ɗaukaka!"

10 Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa;

Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.

11 Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa;

Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.

Veja também

Publicidade
Bíblia Online Bíblia Online

Bíblia Online • Versão: 2026-06-16_18-40-07-