Publicidade

Salmos 65

Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Wata waƙa.

1 Yabo ya dace da kai, ya Allah, a Sihiyona;

a gare ka za mu cika alkawuranmu

2 Ya kai wanda yake jin addu’a

a gare ka dukan mutane za su zo.

3 Sa’ad da zunubai suka sha ƙarfinmu,

ka gafarta laifofinmu.

4 Masu albarka ne waɗanda ka zaɓa

ka kawo kusa don su zauna a filayenka!

Mun cika da abubuwa masu kyau na gidanka,

na haikalinka mai tsarki.

5 Ka amsa mana da ayyuka masu banmamaki na adalci,

Ya Allah Mai Cetonmu,

begen dukan iyakar duniya

da kuma na tekuna masu nesa,

6 wanda ya yi duwatsu ta wurin ikonka,

bayan ka kintsa kanka da ƙarfi,

7 wanda ya kwantar da rurin tekuna,

rurin raƙumansu,

da kuma tumbatsar al’ummai.

8 Waɗanda suke zama can da nesa sukan ji tsoron manyan ayyukanka;

inda safe ke haskaka yamma kuma ta shuɗe

kakan sa a yi waƙoƙin farin ciki.

9 Kana kula da ƙasa kana kuma yi mata banruwa;

kana azurta ta a yalwace.

Rafuffukan Allah sun cika da ruwa

don su ba mutane hatsi,

don haka ne ka ƙaddara.

10 Ka kwarara ta da ruwa ka kuma baje kunyoyinta;

ka sa ta yi laushi da yayyafi ka kuma albarkaci tsire-tsirenta.

11 Saboda alherinka, ya Allah, an sami kaka mai albarka,

amalankenka kuwa sun cika har suna zuba.

12 Makiyayan hamada sun cika har suna zuba;

tuddai sun rufu da murna.

13 Wurin dausayin kiwo sun rufu da garkuna

kwari kuma sun cika da hatsi;

suna sowa don farin ciki.

Veja também

Publicidade
Bíblia Online Bíblia Online

Bíblia Online • Versão: 2026-06-16_06-50-08-