Publicidade

Salmos 16

Miktam ne na Dawuda.

1 Ka kiyaye ni, ya Allah,

gama a cikinka nake samun mafaka.

2 Na ce wa Ubangiji, "Kai ne shugabana;

in ba tare da kai ba, ba ni da wani abu mai kyau."

3 Game da tsarkakan da suke cikin ƙasar kuwa,

su ne masu ɗaukakar da dukan farin cikina ya dangana.

4 Baƙin ciki zai ƙaru wa waɗanda suke bin waɗansu alloli.

Ba zan zuba musu hadayarsu ta jini ba

ko in ambaci sunayensu da bakina.

5 Ubangiji, ka ba ni rabona da kwaf ɗin na;

ka kiyaye rabona,

6 Iyakoki sun fāɗo mini a wurare masu daɗi;

tabbatacce ina da gādo mai bansha’awa.

7 Zan yabi Ubangiji, wanda yake ba ni shawara;

ko da dare ma zuciyata kan koya mini.

8 Kullum nakan sa Ubangiji a gabana.

Gama yana a hannun damana, ba zan jijjigu ba.

9 Saboda haka zuciyata tana murna harshena kuma yana farin ciki;

jikina kuma zai zauna lafiya,

10 domin ba za ka yashe ni a kabari ba,

ba kuwa za ka bar Mai Tsarkinka yă ruɓa ba.

11 Ka sanar da ni hanyar rai;

za ka cika ni da farin ciki a gabanka,

da madawwamin jin daɗi a hannun damarka.

Veja também

Publicidade
Bíblia Online Bíblia Online

Bíblia Online • Versão: 2026-06-16_18-40-07-