Pular para o conteúdo
Publicidade

Salmos 125

Waƙar haurawa.

1 Waɗanda suke dogara ga Ubangiji suna kama da Dutsen Sihiyona,

wanda ba ya jijjiguwa amma dawwammame ne har abada.

2 Kamar duwatsun da sun kewaye Urushalima,

haka Ubangiji ya kewaye mutanensa

yanzu da har abada kuma.

3 Sandar mulkin mugaye ba zai ci gaba da kasance

a kan ƙasar da take rabon adalai ba,

domin kada masu adalci su yi amfani

da hannuwansu su aikata mugunta.

4 Ka yi alheri, ya Ubangiji, ga waɗanda suke nagartattu,

ga waɗanda suke masu aikata gaskiya a zuciyarsu.

5 Amma waɗanda suka juye ga karkatattun hanyoyi

Ubangiji zai kore su tare da masu aikata mugunta.

Salama kasance tare da Isra’ila.

Veja também