1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji dutsena,
wanda ya horar da hannuwana don yaƙi,
yatsotsina don faɗa.
2 Shi ne Allah mai ƙaunata da kuma kagarata,
katangata da mai cetona,
garkuwata, wanda nake neman mafaka daga gare shi,
wanda ya sa mutane a ƙarƙashina.