6 Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini;
ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
7 Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki,
kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu
da hannunka na dama.
8 Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido;
ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
9 daga mugaye waɗanda suke kai mini hari,
daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.