22 Zan furta sunanka ga ’yan’uwana;
cikin taron masu sujada zan yabe ka.
23 Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi!
Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi!
Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
24 Gama bai rena ko yă ƙyale
wahalar masu shan wuya ba;
bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba
amma ya saurari kukansa na neman taimako.