1 Zan girmama ka Ya Ubangiji,
gama ka tsamo ni daga zurfafa
ba ka bar abokan gābana sun yi farin ciki a kaina ba.
2 Ya Ubangiji Allahna, na yi kira gare ka don taimako
ka kuwa warkar da ni.
3 Ya Ubangiji, ka dawo da ni daga kabari;
ka kiyaye ni daga gangarawa zuwa cikin rami.