1 A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka;
kada ka bari in taɓa shan kunya;
ka cece ni cikin rahamarka.
2 Ka juye kunnenka gare ni,
ka zo da sauri ka cece ni;
ka zama dutsen mafakata,
mafaka mai ƙarfi na cetona.
3 Da yake kai ne dutsena da kuma kagarata,
saboda sunanka ka bi da ni ka kuma jagorance ni.
4 Ka ’yantar da ni daga tarkon da aka sa mini,
gama kai ne mafakata.
5 Cikin hannuwanka na miƙa ruhuna;
ka cece ni, ya Ubangiji Allah na gaskiya.