1 Mai farin ciki ne shi
wanda aka gafarta masa laifofinsa,
wanda aka shafe zunubansa.
2 Mai farin ciki ne mutumin
da Ubangiji ba ya lissafin zunubinsa a kansa
wanda kuma babu ruɗu a ruhunsa.
3 Sa’ad da na yi shiru,
ƙasusuwana sun yi ta mutuwa
cikin nishina dukan yini.
4 Gama dare da rana
hannunka yana da nauyi a kaina;
an shanye ƙarfina ƙaf
sai ka ce a zafin bazara. Sela
5 Sa’an nan na furta zunubina a gare ka
ban kuwa ɓoye laifina ba.
Na ce, "Zan furta
laifofina ga Ubangiji."
Ka kuwa gafarta
laifin zunubina. Sela
6 Saboda haka bari duk mai tsoron Allah yă yi addu’a gare ka
yayinda kake samuwa;
tabbatacce sa’ad da manyan ruwaye suka taso,
ba za su kai wurinsa ba.