Pular para o conteúdo
Publicidade

Salmos 32

1 Mai farin ciki ne shi

wanda aka gafarta masa laifofinsa,

wanda aka shafe zunubansa.

2 Mai farin ciki ne mutumin

da Ubangiji ba ya lissafin zunubinsa a kansa

wanda kuma babu ruɗu a ruhunsa.

3 Sa’ad da na yi shiru,

ƙasusuwana sun yi ta mutuwa

cikin nishina dukan yini.

4 Gama dare da rana

hannunka yana da nauyi a kaina;

an shanye ƙarfina ƙaf

sai ka ce a zafin bazara. Sela

5 Sa’an nan na furta zunubina a gare ka

ban kuwa ɓoye laifina ba.

Na ce, "Zan furta

laifofina ga Ubangiji."

Ka kuwa gafarta

laifin zunubina. Sela

6 Saboda haka bari duk mai tsoron Allah yi addu’a gare ka

yayinda kake samuwa;

tabbatacce sa’ad da manyan ruwaye suka taso,

ba za su kai wurinsa ba.

Veja também