1 Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
2 Ku rera ɗaukaka ga sunansa;
ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
3 Ku ce wa Allah, "Ayyukanka da banmamaki suke!
Ikonka da girma yake
har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
4 Dukan duniya sun rusuna a gabanka
suna rera yabo gare ka,
suna rera yabo ga sunanka." Sela