1 Ya mutanena, ku ji koyarwata;
ku saurari kalmomin bakina.
2 Zan buɗe bakina da misalai,
zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
3 abin da muka ji muka kuma sani,
abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
4 Ba za mu ɓoye su wa ’ya’yanmu ba;
za mu faɗa wa tsara mai zuwa
ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji,
ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.