9 Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta?
Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
10 Na neme ka da dukan zuciyata;
kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
11 Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata
don kada in yi maka zunubi.
12 Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji;
ka koya mini ƙa’idodinka.
13 Da leɓunana na ba da labarin
dukan dokokin da suka fito bakinka.
14 Na yi farin ciki da bin farillanka
yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
15 Na yi tunani a kan farillanka
na kuma lura da hanyoyinka.
16 Na yi murna a cikin ƙa’idodinka;
ba zan ƙyale maganarka ba.
ג Gimel