1 Ya Ubangiji, ka bincike ni
ka kuwa san ni.
2 Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi;
ka san tunanina daga nesa.
3 Ka san fitata da kuma kwanciyata;
ka saba da dukan hanyoyina.
4 Kafin in yi magana da harshena
ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.