6 Yanzu na san cewa,
Ubangiji yakan cece shafaffensa.
Yakan amsa masa daga samansa mai tsarki
da ikon ceto na hannun damansa.
7 Waɗansu sun dogara a kekunan yaƙi waɗansu kuma a dawakai,
amma mu, mun dogara a cikin sunan Ubangiji Allahnmu.
8 Za a durƙusar da su, su kuma fāɗi,
amma mu za mu tashi mu tsaya daram.