5 Ka nemi hutu, ya raina, a wurin Allah kaɗai;
dogarata kan zo daga gare shi ne.
6 Shi ne kaɗai dutsena da cetona;
shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
7 Cetona da girmata sun dangana ga Allah ne,
shi ne dutsena mai ƙarfi, mafakata.
8 Ku dogara a gare shi a duk lokuta, ya mutane;
ku faɗi albarkaci bakin zukatanku a gare shi,
gama Allah ne mafakarmu. Sela